Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Ndume: a bayyana sunayen ‘yan canjin da ake zargi da daukar nauyin boko haram

Published

on

Shugaban kwamitin kula da rundunar sojin kasar nan na majalisar dattijai sanata Ali Ndume, ya bukaci gwamatin tarayya da ta bayyana sunayen masu sana’ar canjin kudaden kasashen waje wadanda ake zarginsu da alaka da kungiyar boko haram.

 

A baya-bayan nan ne dai jami’an tsaro suka kama wasu masu canjin kudaden ketare da ake zargin suna samar da kudade ga kungiyar boko haram.

 

Sanata Ali Ndume ya bayyana hakan ne yayin zantawa da manema labarai a Abuja.

 

Ya ce halin da ake ciki a wannan lokaci, akwai bukatar gwamnati ta tashi haikan wajen daukar tsastsauran mataki akan duk wani mai neman tada zaune tsaye a kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!