Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NEMA ta shawarci gwamnoni su kafa cibiyoyin ba da agajin gaggawa

Published

on

Hukumar ba da agajin gaggawa NEMA, ta shawarci gwamnonin Nijeriya da su kafa kananan cibiyoyin ba da agajin gaggawa, tare da karfafa ayyukan hukumomin ba da agaji na jihohinsu domin dakile afkuwar ambaliyar ruwa a damunar bana.

Darakta Janar na hukumar Mustapha Habib Ahmad, ne ya bayar da shawarar a ganawarsa da manema labarai a birnin tarayya Abuja, bayan kammala ganawa da kungiyar gwamnonin Nijeriya NGF.

Mustapha Habib, ya ce, akwai bukatar gwamnonin su dauki wannan mataki domin dakile afkuwar annobar ambaliyar ruwa da ke addabar wasu jihohi da dama.

Haka kuma, Ya kara da cewa matukar gwamnonin suka hada kai da hukumar NEMA, to hakika akwai yiwuwar rage tasirin barnar da amlabiyar ruwa ke yi da kaso mai girma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!