Connect with us

Labaran Wasanni

NFF ta alakanta jinkirin biyan albashin ‘yan wasa da annobar Corona

Published

on

Hukumar kwallon kafa ta kasa NFF ta alakanta tsaikon da aka samu na rashin biyan ‘yan wasa da masu horarwa kudadensu akan lokaci da matsalar karancin kudaden shiga da annobar Corona ta haifar a kasar.

Barkewar cutar Corona dai ya sanya harkokin wasanni da kasuwanci tsayawa cak a fadin duniya a shekarar da ta gabata, lamarin da hukumar ta ce ya kawo mata tsaiko ta fannin karancin kudaden gudanarwa.

A wata tattaunawa da mai tsaron bayan kungiyar kwallon kafa ta Najeriya Leon Balogun yayi da manema labarai, ya bayyana yadda ‘yan wasan da masu horarwa ke bin hukumar bashin kudaden da dama.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!