Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Nijeriya ta yi watsi da rahoton EU

Published

on

Gwamnatin tarayya ta yi watsi da rahoton ƙungiyar Tarayyar Turai EU game da sakamakon babban zaɓen bana, da ya bai wa Bola Ahmed Tinubu nasarar zama shugaban ƙasa.

Cikin rahoton nata, ƙungiyar ta ce, sunan hukumar zaɓen Nijeriya INEC ya baci, musamman saboda gazawa wajen ɗora sakamakon zaben shugaban ƙasa a shafin Intanet, a lokacin da ta yi alƙawari tun da farko.

Wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasa ta bayyana rahoton a matsayin “maras kan-gado, da aka haɗa shi ta hanyar dogaro da abubuwan da suka faru a rumfunan zaɓe ƙasa da Dubu 1 cikin Dubu 176, da aka kaɗa ƙuri’a” a ranar zaɓen na watan Fabrairu.

Sai dai har yanzu jam’iyyun adawa na PDP da Labour na ci gaba da ƙalubalantar sakamakonsa a gaban kotu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!