Labarai
NLC ta ayyana goyon baya ga yajin aikin da Ƙungiyar NUT ke yi

Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC ta ayyana goyon bayanta ga yajin aikin da mambobin Kungiyar Malamai ta NUT ke yi a halin yanzu sakamakon tabarbarewar tsaro da kuma yawaitar sace malamai da dalibai.
A cikin wata sanarwa da shugaban NLC, Joe Ajaero, ya fitar a Daren jiya Laraba, ya ce yajin aikin ya nuna irin gajiyar da malamai suka yi sakamakon hare-haren da ake ci gaba da kai musu, musamman a wuraren da ke fuskantar barazanar tsaro.
Ya bayyana cewa wasu abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, ciki har da sace daliban makaranta a Jihar Oyo, sun kara nuni da yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara a fadin kasar nan.
Ajaero ya ce akwai bukatar gwamnati ta dauki matakan gaggawa domin kare rayuka da dukiyoyin malamai da dalibai, tare da samar da yanayin da zai ba da damar gudanar da harkokin ilimi cikin kwanciyar hankali.
You must be logged in to post a comment Login