Labarai
ADC ta zargi Shugaba Tinubu da nuna wariya

Jam’iyyar ADC a Jihar Kano ta zargi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da nuna wariya wajen tafiyar da harkokin tsaro tsakanin Arewa da Kudu.
Shugaban jam’iyyar na jihar, Musa Ungoggo, ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce matakin gaggawar da gwamnatin tarayya ta ɗauka domin ceto mutane 40 da aka yi garkuwa da su a Jihar Oyo ya bambanta da yadda ake mayar da martani ga hare-haren da ke faruwa a jihohin Arewa.
Musa Ungoggo ya yi nuni da hare-haren da suka jawo asarar rayuka a jihohin Plateau, Kaduna, Sokoto, Zamfara, Katsina da Neja, yana mai cewa al’ummomin Arewa sun daɗe suna fuskantar matsalolin tsaro ba tare da samun irin kulawar da gwamnatin tarayya ta nuna a Oyo ba.
Ya kuma zargi fadar shugaban ƙasa da tafiyar da tsarin tsaro da ke fifita wasu yankuna fiye da wasu, lamarin da ya ce na iya haifar da rarrabuwar kawuna a ƙasa.
Jam’iyyar ADC ta buƙaci Shugaba Tinubu da ya faɗaɗa irin matakan tsaron da aka ɗauka a Oyo zuwa jihohin Arewa da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga da masu tayar da kayar baya, tare da ƙara tura jami’an tsaro da masu gadin dazuka domin magance matsalar.
You must be logged in to post a comment Login