Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NLC ta baiwa gwamnati wa’adin makonni biyu ta janye karin farashi

Published

on

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa NLC ta baiwa gwamnatin tarayya wa’adin makonni biyu na ta janye ƙarin farashin wutar lantarki da na man fetur da ta yi.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwar bayan taro da masu ruwa da tsaki a ƙungiyar suka gabatar, wadda ta fitar a yammacin jiya laraba, mai ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa Kwamared Ayuba Wabba.
Jim kaɗan bayan sanarwar, wakilinmu Nasir Salisu Zango ya zanta da shugaban ƙungiyar na ƙasa reshen jihar Kano, Kwamared Kabiru Ado Minjibir wanda ya ce, daukar wannan mataki ya zama tilas.
A farkon watan Satumban da muke ciki ne dai gwamnatin tarayya ta yi ƙarin farashin wutar lantarki da kuma na man fetur wanda ya janyo cece-kuce a ƙasar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!