Connect with us

Labarai

PDP ta sauya dan takararta na gwamnan Kano

Published

on

Shugaban Jam’iyyar PDP na jihar Kano, Injiniya Bello Gambo Bichi, ya sanar da sauya ɗan takarar jam’iyyar na gwamnan Kano a zaben 2027.

 

Hakan ya biyo bayan janyewar da Muhammad Bello Dalha ya yi daga takarar, inda kuma jam’iyyar ta maye gurbinsa da Muhammad Sani Abacha, sakamakon masalahar da aka cimma tsakanin ɓangarorin jam’iyyar.

A yayin wani taron manema labarai da jam’iyyar ta gudanar, Muhammad Bello Dalha, ya bayyana cewa, ya janye daga takarar ne bisa radin kansa, bayan an cimma masalaha tare da samun goyon bayan shugabannin jam’iyyar na ƙananan hukumomi 44 na Kano.

 

Taron dai, ya samu halartar wakilan hukumar zaɓe INEC, da kuma shugabannin kwamitocin zaɓe na jam’iyyar PDP.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!