Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

NNPC:ya sanya hannu kan takardar fahimtar juna da jami’ar Bayero

Published

on

Kamfanin mai na kasa NNPC ya sanya hannu kan takardar fahimtar juna don gina babban sashen nazarin Civil Engineering a jami’ar Bayero dake nan Kano.

Ana sa ran aikin ginin zai lakume kudi da ya fiye da naira milyan dari uku da casa’in da bakwai.

Uban jami’ar Farfesa Muhammad Yahuza Bello da ya samu wakilcin mataimakin san a harkokin mulki Farfesa Haruna Wakili yay aba da kokarin kamfanin mai na kasa NNPC da suka jima suna bukatar hakan, inda yace jami’ar zata ci gaba da yin hadaka da NNPC wajen ciyar da jami’ar gaba.

Farfesa Haruna Wakili ya kuma bukaci ‘yan kwangilar dasu maida hankali wajen yin aiki mai nagarta kamar yadda aka san jami’ar wajen yin sabbin gine-gine masu inganci.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!