Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za’a mayar da NNPC hannun ‘yan kasuwa- Mele Kyari

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce za ta mika ragamar gudanar da harkokin matatun man kasar nan ga bangarori masu zaman kansu da zarar an kammala gyaran da ake yi musu.

Shugaban kamfanin mai na kasa NNPC Malam Mele Kyari ne ya bayyana haka yayin zantawa da wani gidan talabijin.

Ya ce idan an kammala garambawul da ake yi ga matatun man kamfanin NNPC zai shiga yarjejeniya da bangarorin masu zaman kansu wadanda za su karbe ragamar kula da matatun man.

LABARAI MASU ALAKA

Kamfanin NNPC ya tallafawa asibitin Aminu Kano

NNPC zai fara aikin yashe tafkin Chadi da ya Santana ruwa yankin Gongola

NNPC:ya sanya hannu kan takardar fahimtar juna da jami’ar Bayero

Malam Mele Kyari ya kuma ce kamfanin NNPC zai daina kula da matatun man maimamakon haka zai cimma yarjejeniya da bangarorin masu zaman kansu wadanda za su zuba jari sannan su rika kula da harkokinsu na Kyau nda kullum.

A cewar sa daukar wannan mataki ya zama wajibi domin tsawon shekaru gwamnati na kashe makudan kudade wajen kula da matatun man sai dai a wannan lokaci akwai bukatar sake salo domin farfado da matatun su rika biyan bukatun da yasa aka kafa su tun da fari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!