Labarai
NNPP ta ce ba za ta tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027 ba

Jam’iyyar NNPP ta sanar da cewa ba za ta tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027 ba, tana mai cewa burinta shi ne haɗa kan jam’iyyun adawa domin ceto ƙasar daga matsalolin da take fuskanta.
Jaridar TheCable ta rawaito cewa, shugaban jam’iyyar na ƙasa, Bala Yusuf, ya bayyana hakan ne a taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) da aka gudanar a Abuja, inda ya ce NNPP a shirye take ta kulla ƙawance da kowace jam’iyya da ta fito da ɗan takara nagari kuma mai hangen nesa.
Ya kuma musanta rahotannin da ke cewa jam’iyyar ta riga ta shiga wata haɗaka da wasu jamiyyun siyasa, ciki har da African Democratic Congress (ADC), yana mai cewa za su fara tantance ‘yan takarar da sauran jam’iyyu za su gabatar kafin yanke shawarar wanda za su mara wa baya.
Matakin na NNPP ya zo ne bayan ficewar manyan jiga-jiganta daga jam’iyyar, ciki har da Rabiu Musa Kwankwaso, Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, da wasu zaɓaɓɓun jami’ai.
You must be logged in to post a comment Login