Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya tura tawaga zuwa Oyo bayan sace ɗalibai da malamai

Published

on

Shugaba Bola Tinubu ya tura wata babbar tawaga ta gwamnati zuwa ƙauyukan Esiele da Yawota da ke yankin Ogbomoso a Jihar Oyo bayan sace ɗalibai da malamai kusan 46.

A cewar Jaridar DailyPost, tawagar ta ƙunshi Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu, da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Tunde Disu.

Sauran mambobin tawagar sun haɗa da Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa; Ministan Wutar Lantarki, Joseph Tegbe; da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Hulɗa da Jama’a, Sunday Dare.

Tun da fari dai wasu ƴan ta’adda sun kai hare-hare lokaci guda a makarantu biyu na Baptist Nursery da Primary School inda suka yi garkuwa da ɗalibai da malamai kusan 46.

A gefe guda kuma Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da daukar masu gadin daji 1,000 a jihar Oyo, tare da umartar rundunar tsaro ta musamman mai kwarewa a ayyukan ceto ta kara kaimi wajen kubutar da dalibain.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!