Connect with us

Labarai

Al’hazan jihar Jigawa zasu fara dawowa gida Najeriya a mako mai zuwa

Published

on

Mahajjatan Jihar Jigawa da suka halarci aikin Hajjin 2026 za su fara komawa gida daga ranar 6 ga watan Yuni, kamar yadda Amirul Hajj na jihar kuma Sarkin Dutse, Muhammad Hameem Nuhu Sunusi, ya sanar. Ya bayyana hakan ne yayin ziyarar da ya kai wa mahajjatan jihar da ke zaune a Makkah bayan kammala ibadun Hajji.

Sarkin ya yaba wa mahajjatan bisa yadda suka nuna ladabi, haƙuri da bin dokokin aikin Hajji, tare da ƙarfafa musu gwiwar ci gaba da kiyaye dokokin jiragen sama yayin shirye-shiryen komawa gida. Ya kuma gargade su da kada su wuce adadin kayan da aka amince su ɗauka domin kauce wa matsaloli a filin jirgin sama.

Haka kuma, ya taya su murnar samun damar cika ɗaya daga cikin rukunnan Musulunci guda biyar, tare da roƙonsu da su ci gaba da yi wa Jihar Jigawa da Najeriya addu’o’in zaman lafiya, haɗin kai, ci gaba da samun shugabanci nagari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!