Connect with us

Labarai

Obasanjo ya yi suka kan albashi da kuɗaɗen da ƴan majalisar tarayya ke karɓa

Published

on

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya soki albashi da kuɗaɗen gudanarwa da ’yan majalisar tarayya ke karɓa, yana mai cewa bai dace a rinka biyansu wadannan kudaden ba a ƙasar da ake biyan mafi ƙarancin albashi na N70,000.

Obasanjo Ya zargi ’yan majalisar da tsara yanayin albashinsu da kansu, wanda ya ce ya sabawa kundin tsarin mulkin ƙasar. Ya bayyana hakan ne a jiya Lahadi a wata tattaunawa ta yanar gizo ta The Toyin Falola Interviews, karkashin jagorancin Toyin Falola.

A wajen taron, an kuma samu mahalarta irin su The Kukah Centre wanda Matthew Kukah ya wakilta, da tsohon dan takarar shugaban ƙasa Kingsley Moghalu, yayin da Obasanjo ya kwatanta kasafin majalisar yanzu da na 2007, yana cewa bambancin yana da yawa kuma abin mamaki ne.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!