Connect with us

Labarai

PDP ta dakatar da wasu mambobin ta a jihar Kano

Published

on

Shugaban Jam’iyyar PDP reshen Jihar Kano, Alhaji Yusuf Ado Kibya, ya sanar da dakatar da mambobi uku na jam’iyyar bisa zargin aikata laifukan da suka sabawa kundin tsarin PDP da manufofinta. A cikin sanarwar da ya fitar a jiya talata, ya ce jam’iyyar ta gano wasu ayyuka, dabi’u da halaye daga wasu mambobi da suka karya doka da oda, ciki har da shiga harkokin jam’iyyar adawa, aikata ayyukan da ka iya zubar da mutuncin jam’iyyar, da kuma aikata almundahana.

 

Alhaji Yusuf Ado Kibya ya bayyana cewa, a wani taro da kwamitin zartarwar jam’iyyar PDP Kano ya gudanar a ranar 15 ga Disamba, 2025, an yanke shawarar dakatar da mambobin uku gabanin kammala bincike da ɗaukar mataki na ƙarshe. Wadanda abin ya shafa sun hada da Ibrahim Bala Aboki daga Karamar Hukumar Nassarawa, Injiniya Bello Gambo Bichi daga Karamar Hukumar Bichi, da Rabiu Wangal daga Karamar Hukumar Nassarawa. Ya ce an dakatar da su nan take bisa tanadin sashe na 58  na kundin tsarin PDP da aka yi wa gyara a shekarar 2017.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!