Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Siyasar Kano: Dalilan korar Kwankwaso daga PDP

Published

on

Jam’iyyar PDP tsagin Alhaji Aminu Wali ta bayyana dalilan da suka sanya ta dakatar da tsohon gwamnan Kano Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso daga jam’iyyar.

Shugaban jam’iyyar Munhaminna Baƙo Lamiɗo shi ne ya sanar da korar Kwankwaso da ranar Alhamis bayan babban taron jam’iyyar na jiha.

Lamiɗo ya ce, an dakatar da shi ne saboda zargin yiwa jam’iyyar zagon ƙasa, da kuma haɗa baki da jam’iyya mai ci a matakin ƙasa don samun takara a 2023.

Haka kuma Kwankwason ya haifar da baƙin jini da ƙiyayya a tsakanin ƴan jam’iyyar PDP wanda ya haifar da asarar ɗan majalisar tarayya Ali Datti Yako.

Labarai masu alaka:

Siyasar Kano: An ja layi tsakanin Sha’aban da Ganduje

Siyasar Kano: Ko Baffa Bichi ya ƙwace takarar Abba Gida-Gida?

Lamiɗo ya ƙara da cewa, Kwankwason na karya dokokin jam’iyyar tare da ƙin biyayya ga kwamitin zartarwa na jam’iyyar a Kano.

Abu na ƙarshe ya ce, Kwankwaso yana cin zarafi tare da wulaƙanta shugabannin jam’iyyar na jiha.

Har kawo lokacin haɗa wannan rahoto, jam’iyyar PDP tsagin Kwankwason ba ta ce komai ba game da batun.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!