Siyasa
Peter Obi ya tabbatar ficewa daga jam’iyyar ADC

Tsohon ɗan takarar shugabancin kasar nan a zaɓen 2023 na Jam’iyyar LP, kuma jigo a jam’iyyar ADC ta haɗaka, Peter Obi ya tabbatar ficewa daga jam’iyyar.
Ta cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin sa na X a yau, Peter Obi ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon rigingimun cikin gida dana Kotu da suka dabaibaye jam’iyyar.
Haka zalika ya ce rigimar da ya yi ƙoƙarin guje wa a tsohuwar jam’iyyar sa ta LP, ta sake kunno kai a cikin sabuwar jam’iyyar da ya shiga ta ADC, a yanzu haka.
Obi ya ce ya ɗauki matakin ne ba don wani shugaba ko jigo a cikin ADC ya ɓata masa rai ba.
You must be logged in to post a comment Login