Siyasa
Jam’iyyar hamayya ta ADC ta sanar da fara siyar da fom ɗin takara

Jam’iyyar hamayya ta ADC ta sanar da fara siyar da fom ɗin takara muƙamai daban-daban gabanin babban zaɓen ƙasar na 2027.
Hakan na kunshe cikin sanarwar da kakakin jam’iyyar na ƙasar,Malam Bolaji Abdullahi ya fitar, da ta tabbatar da jam’iyyar ta saka kuɗin fom ɗin takarar shugaban ƙasa akan naira miliyan 100.
Sanarwar ta kuma ce jam’iyyar ta fitar da jadawalin zaɓukan fitar da gwani na jam’iyyar, inda za a yi na shugaban ƙasa ranar 25 ga watan Mayu.
Jam’iyyar ta kuma saka kuɗin fom ɗin takarar gwamna kan naira miliyan 50, yayin da na sanata ke naira miliyan 20, sai na ɗan majalisar tarayya a kan naira miliyan 10 da ɗan majalisar jiha naira miliyan uku.
Sanarwar ta kuma bayyana rangwamen kaso 50 cikin ɗari ga matasa, da ragin kaso 25 ga mata da masu buƙata ta musamman.
You must be logged in to post a comment Login