Siyasa
Fantami ya yi watsi da sansanci kan takarar gwamna a jihar Gombe

Farfesa Isa Ali Pantami ya yi watsi da sasancin da aka yi kan fitar da Jamilu Gwamna takarar Gwamnan jihar Gombe a jamiyyar APC
Wata sanarwa daga bangaren masu goyon bayan Isa Ali Ibrahim Pantami ta bayyana rashin amincewa da abin da suka kira “nadi” domin tsayar da dan takarar Gwamna a jihar Gombe, tana mai cewa hakan ya saba da tanadin dokar zabe ta Nijeriya.
Sanarwar da aka wallafa a shafin Pantamin na Facebook, ta jaddada cewa babu sahihin sasancin consensus sai idan dukkan masu neman takara sun amince a rubuce su janye, idan ba haka ba dole ne jam’iyya ta koma zaben fidda gwani kai tsaye.
You must be logged in to post a comment Login