Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

PSG na bukatar Neymar da Mbappe su kara mata kwantiragi

Published

on

Daraktan wasanni na kungiyar kwallopn kafa ta PSG Leonardo, ya ce, sun fara tattaunawa da ‘yan wasansu Neymar da Kylian Mbappe kan batun kwantiraginsu da kungiyar.

‘Yan wasan gaban guda biyu wadanda PSG ta kashe sama da Yuro miliyan 400 wajen daukosu, kwantiragin na su zai kare a shekarar 2022.

Leonardo ya kuma ce, suna cigaba da tattaunawa batun kwantiragin Angel Di Maria da kuma Juan Bernat.

Haka zalika ya bayyana cewa za a kawo karshe duk wani batu na tsawaita kwantiragin wasu daga cikin ‘yan wasan kungiyar a mako mai kamawa.

Daraktan ya ce “Akwai kyakkyawar alaka tsakani na da Thomas Tuchel don haka bana tinanin canjashi duk da rashin nasarar da muka samu a wasanni biyu cikin uku na farko a gasar Champions League.”

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!