Connect with us

Labaran Wasanni

PSG tayi nasara da ci 1-0 a kan Real Madrid

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint Germain tayi nasarar doke Real Madrid da ci 1-0 a wasan gasar cin kofin zakarun turai Champions League.

Fafatawar da ta gudana a ranar Talata 15 ga Fabrairun 2022 a filin wasa na Parc des Prince da ke kasar Faransa.

'Yan wasan PSP da na Real Madrid

‘Yan wasan PSP da na Real Madrid

Dan wasa Klian Mbappe ne ya zura kwallo daya tilo a ragar Real Madrid a minti na 94 dab da za a tashi daga wasan.

Wasan dai shi ne na farko a zagaye na 16 na kungiyoyin da ke fafatawa a gasar ta kakar wasannin shekarar 2021/2022.

A wasa na gaba dai Real Madri zata karbi bakuncin PSG a filin wasa na Santiago a ranar 9 ga maris mai zuwa.

A daya wasan da aka gudanar dai Manchester City ta lallasa Sporting Lisbon da ci 5-0 a wasan da suka fafata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!