Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Gambo Muhammad ya dawo Kano Pillars a matsayin mataimakin mai horarwa

Published

on

Tsohon dan wasan gaba na kasa Najeriya da Kano Pillars Gambo Muhammad ya zama mataimakin mai horarwa a tawagar Sai Masu Gida.

Gambo Muhammad ya koma Pillars ne bayan kammala karatun aikin horarwa a kwalejin harkokin wasanni ta kasa da ke birnin tarayya Abujua.

Gambo Muhammad a Super Eagles

Tsohon dan wasan zakarun gasar Firimiya ta kasa har sau hudu zai kasance da Pillars har nan da lokaci masu yawa a nan gaba.

Mai magana da yawun kungiyar Rilwanu Idris Malikawa Garu ne ya sanar da hakan, gabannin wasan da Pillars zatayi da Plateau United a gasar NFPL.

Wanda hakan zai bashi damar kasancewa a matsayin mataimakin mai horarwa mai jiran kota kwana a wasan na Plateau da Pillars a wasan mako na 12.

Gambo Muhammad dai ya shafe shekaru da dama a matsayin dan wasa a Kano Pillars FC, inda ya jagoranci tawagar lashe gasar firimiya har hudu, kafin daga bisani ya koma Katsina Utd wanda ya shafe kakar wasanni biyu a can.

Jim kadan bayan amincewa da aiki a tawagar ta Kano Pillars Gambo Muhammad ya godewa shugaban kungiyar Surajo Shuaibu Jambul, wanda ya yi alkarin zai bada gudun mawa domin ci gaban kungiyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!