Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Ranar Lahadi za ayi Sallah a Zaria – Sarkin Zazzau

Published

on

Maimartaba Sarkin Zazzau Alhaji Shehu Idris ya ce ranar Lahadi itace ranar Sallah a garin Zaria.

Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Wazirin Zazzau, Alhaji Ibrahim Aminu da Freedom Radio ta samu a daren Juma’a tace masarautar bata umarci al’umma su ajiye azuminsu a ranar Asabar ba.

Sanarwar ta kara da cewa Sarkin Zazza na umartar al’umma da suyi biyayya ga umarnin mai alfarma Sarkin musulmi wanda shine Allah ya dorawa hakkin bada sanarwar ganin wata, kuma tuni ya sanar za ayi sallah ranar lahadi.

A daren Juma’a ne aka rika yamadidi da wasu rahoronni a kafafan sada zumunta kan cewa Sarkin Zazzau ya bada sanarwar a ajjye azumi ranar Asabar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!