Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ranar Ma’aikata: Ganduje ya yafe wa Malamai bashin kudin mallakar gidaje

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce, ta yafe wa Malaman makarantun da suka shiga tsarin mallakar gidaje ta hanyar biya a hankali daga albashinsu, ragowar kudin da ba su kammala biya ba.

Gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ne ya bayyana hakan a jawabinsa na bikin ranar ma’aikata na bana da aka gudanar a a filin wasa na Sani Abacha da ke unguwar Kofar mata da safiyar yau Litinin.

Ganduje ya kuma gode wa ma’aikatan jihar Kano bisa goyan baya da hadinkai da suka ba shi wajen gudanar da mulki na tsawon shekaru takwas.

A nasa jawabin, shugaban kungiyar Kwadago ta Najeriya reshen jihar Kano kwamared Kabiru Ado Inuwa, ya ce a tasa mahangar matsalar fanshon wadanda ke barin aikin gwamnati sun fi wanda ake dauka yawa.

Taron dai, ya samu halartar kungiyoyin ma’aikata daga bangaren gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu.

 

Rahoton: Abba Isah Muhammad

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!