Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ranieri ya zama Mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Watford

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Watford ta sanar da nada Claudio Ranieri a matsayin sabon mai horas da ‘yan wasan kungiyar, domin maye gurbin Xisco Munoz wanda ta sallama a ranar Lahadi.

Dan kasar Italiya, mai shekaru 69 ya koma horas da ‘yan wasa a gasar a Primiyar kasar Ingila ne, bayan rawar da ya taka a Leicester City a tsakanin shekarar 2015 da 2016, wanda ya bar Sampdoria tun kan fara kakar wasanni ta bana.

Claudio Ranieri shine mai horaswa na goma 14 da kungiyar ta Watford ta dauka tun bayan da iyalan Pozzo suka mallaki kungiyar a shekar 2012.

An umarci Ranieri da ya bunkasa wasannin kungiyar da take fafatawa a gasar Primiyar kasar Ingila, wadda take ta 14 a kasan teburi da maki bakwai bayan data buga wasa bakwai.

Wasan farko da Ranieri zai jagoranci kungiyar shine wanda za ta karbi bakuncin Liverpool ranar Asabar 16 ga watan da muke ciki.

Masana harkokin kwallon kafa a kasar Ingila na ganin Ranieri yana da gogewar da zai iya daga martabar Watford.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!