Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rashin magance kananan cututtuka shine ke kawo manya -Likita

Published

on

Shugaban sashen nazarin lalurar koda na asibitin koyarwa na Aminu Kano Saminu Muhammad ya ce, rashin magance kananan cututtuka da ke addabar al’umma da wuri na daga cikin dalilan dake kara haddasa yaduwar manyan cututtuka ga mutane.

Malam Saminu Muhammamd, ya bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala shirin barka da hantsin na nan tashar freedom rediyo wanda ya mayar da hankali kan ciwon Koda.

Ya ce, cututtuka irin su hawan jini da amai da gudawa da kuma ciwon siga suna daga cikin lalurar da ke haifar da ciwon Koda.

LABARAI MASU ALAKA

Cutar ciwon kunne na raguwa sakamon wayar da kan al’umma- Likita

Asalin cutar Tamowa na afkuwa ne tun kafin a haifi jariri- Likita

AKTH ya samu nasarar gudanar da aikin kwakwalwa karo na biyu

A nasa bangaren wani malamin jinya a asibitin koyarwa na Aminu Kano, Malam Mustapha Adam ya ce, kamata ya yi duk mutumin da ya ke dauke da wannan lalura, ya san irin abubuwan da ya kamata ya rika yi don kare kansa daga kara ta’azarar cutar.

Bakin dai sun kuma yi kira ga jama’a da su rika ziyartar asibiti akai-akai don yin gwaji, ba lallai sai sun ji basu da lafiya ba

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!