Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Akwai barazanar kamuwa da cutar sukari saboda rashin wasu sinadarai – Likita

Published

on

Daga Safarau Tijjani Adam

 

Farfesa Ibrahim Danjummai ya ce rashin samun wasu sinadarai a jikin mutum na taka muhimmiyar rawa wajen haddasa ciwon suga a jikin dan adam.

Kwararren likita a sashen kula da masu ciwon suga wato Diabetes da ke asibitin koyarwa na Aminu Kano ne ya bayyana ta cikin shirin “Barka da Hantsi” na nan Freedom Radio.

Ya ce ko wane mutum zai iya kamuwa da ciwon suga, musamman yadda a yanzu ciwon ke kama kananan yara.

Farfesa Ibrahim Danjummai na yin wannan jawabi ne a wani bangare na bikin ranar masu fama da ciwo suga ta duniya.

Ita kuwa jami’ar jinya a asibitn koyarwa na Aminu Kano Hajiya Hauwa Ibrahim ta ce rashin motsa jiki na taka muhimmiyar rawa wajen kawo ciwon suga.

Jami’an biyu sun shawarci jama’a da su rinka zuwa asibiti ana duba lafiyarsu a ko da yaushe domin sanin matakin lafiyarsu.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!