Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Siyasa

Rikici ya barke tsakanin jam’iyyun NNPP da APC a Katsina

Published

on

Rikici ya kaura a jihar Katsina tsakanin magoya bayan jam’iyyun APC mai mulki da kuma ta NNPP mai adawa.

Rahotonni sun bayyana cewa, rikicin ya barke ne sakamakon gano shugaban jam’iyya da kuma dan takara mataimakin gwamna na jami’aryar NNPP cikin taron gangamin neman zabe na jami’yyar APC.

A cewar Dantakarar gwamnan na NNPP a jihar Muhammad Nura Khalil, ya ji raderadin cewa ana so a cefanar da magoya bayan jam’iyyar ta ga jam’iyyar APC.

Dan takarar mataimakin gwamna da shugaban jam’iyyar NNPP sunje je wurin taron yan Jam’iyyar APC wanda hakan ya hasala magoya bayan NNPP din suka fara bore.

Dan takara mataimakin gwamnan Mutaka Rabe Darma ya ce, ya ajiye takararsa inda ya koma jam’iyyar APC.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!