Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Jigawa

Rikicin Siyasa: Ƴan sanda sun yiwa shalkwatar APC ƙawanya a Jigawa

Published

on

Jami’an tsaro a jihar Jigawa sun kewaye sakatariyar jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Rahotonni sun ce, an wayi gari da ganin jami’an tsaro a kan hanyoyin zuwa sakatariyar jam’iyyar da ke birnin Dutse.

Freedom Radio ta tuntuɓi mai magana da yawun rundunar ƴan sanda ta jihar Jigawa SP. Abdu Jinjiri wanda ya ce, sun girke ƴan sandan ne saboda wasu bayanan sirri da suka samu na yiwuwar afkuwar wani lamari a sakatariyar.

A ranar Litinin da ta gabata ne, gwamnan jihar Alhaji Badaru Abubakar ya jagoranci zama da masu ruwa da tsaki a jam’iyyar ta APC a fadar gwamnatin jihar, wanda a yayin taron aka da dakatar da shugaban jam’iyya na jihar Alhaji Habibu Sani Sara.

Sai dai kwanaki biyu da wannan taro Alhaji Habibu Sara ya sanar da manema labarai cewa har yanzu shi ne shugaban jam’iyyar APC a jihar.

Habibu Sara ya yi zargin cewa an bijiro masa da wannan batu ne saboda tarayyar sa da wasu mutane da gwamnatin jihar ba ta jituwa da su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!