Connect with us

Labarai

Rundunar Sojin Sama ta gargadi yan ta’addan da suka addabi Zamfara

Published

on

Rundunar  Sojin Saman Najeriya, ta gargadi  ƴan ta’addan da ke addabar jihohin Zamfara da Katsina da Kebbi da Sokoto da su gaggauta barin maboyar su tare  da mika kan su ko kuma su fuskanci matsanancin farmaki daga jiragen yaki.

 

Wannan gargadi ya zo ne kasa da mako guda bayan rundunar ta yi luguden wuta ta sama kan sansanonin ƴan ta’adda a wasu kauyuka na jihar Zamfara.

 

Da yake jawabi a jiya Laraba yayin gudanar da Faretin soji na musamman a birnin tarayya Abuja, Shugaban Sojin Saman, Air Marshal Hassan Abubakar, ya ce dakarun  za su ci gaba da binciko maboyar waɗannan miyagun mutane tare da kawar da su baki ɗaya.

 

Haka kuma, ya ce, rundunar za ta ci gaba da kare sararin samaniyar kasar tare da ba da gudummowa da hadin gwiwar jami’an tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyi al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!