Labarai
Rundunar Sojoji ta ceto mutane 31 da aka yi garkuwa da su tare da halaka ’yan ta’adda biyar

Rundunar Sojojin kasar nan ta Operation FANSAN YAMMA, ta ceto mutane 31 da aka yi garkuwa da su, tare da halaka ’yan ta’adda biyar yayin wasu atisaye da ta gudanar a jihohin Zamfara da Katsina.
Mai magana da yawun rundunar sojin, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ne ya tabbatar da hakan, ya na mai cewa dakarun za su ci gaba da kai hare-hare domin murƙushe ta’addanci tare da dawo da zaman lafiya a shiyyar Arewa maso Yamma.
Haka kuma, ya ce, an ceto mutane 31 din ne a yankin Bagega zuwa Kawaye da ke ƙaramar Hukumar Anka ta jihar Zamfara bayan jefa bama-bamai daga jiragen yaƙi a maɓoyar ’yan ta’addan a Dajin Bagega.
Haka kuma, ya kara da cewa, waɗanda aka ceto sun shafe tsawon makonni da dama a tsare, kuma ’yan asalin ƙananan hukumomin Maga da Gummi da Zuru da Wasugu da Bukuyyum da kuma Anka ne da ke jihohin Zamfara da Sokoto.
You must be logged in to post a comment Login