Labarai
A saki ɗalibai da malaman da aka sace a Oyo da Borno – MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi kira da a saki ɗalibai da malaman da aka sace a Oyo da Borno a hare-haren da suka faru a jihohin.
Mai kula da ayyukan Majalisar Ɗinkin Duniya da na jin ƙai a kasar nan Mohamed Malick Fall, ne ya bayyana hakan a ganawarsa da tawagar Cibiyar Kula da Tsaron Makarantu ta Ƙasa a birnin tarraya Abuja, ƙarƙashin jagorancin Dakta Samuel Umanah.
A cewarsa, bai kamata a ci gaba da zuba ido ana ganin matsalar tsaro na ci gaba da yiwa makarantu barazana a faɗin ƙasar nan, yana mai cewa irin waɗannan hare-hare na kawo cikas ga ilimi da kariyar yara.
Ya ce makarantu ya kamata su kasance wuraren ilimi masu aminci, ba wuraren tsoro ba, yana mai jaddada cewa bai kamata yara su zama abin hari ba.
You must be logged in to post a comment Login