Labaran Kano
Rundunar ‘Yan sanda a Kano zata kara kaimi kan yaki da aikata laifuka

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta ce za ta ci gaba da haɗa kai da sauran hukumomin tsaro da kuma al’umma, domin tabbatar da zaman lafiya da magance matsalolin tsaro a jihar.
Mataimakin Kwamandan ’yan sandan Ofishin ’yan sanda na yankin Sharada, DSP Muhammad Lawan, ne ya bayyana haka a wani taro da kwamitin tsaro na yankin Rinji Ja’en, da ke unguwar Sharada a ƙaramar hukumar Gwale ta jihar Kano.
DSP Muhammad Lawan ya ƙara da cewa wajibi ne iyaye su ɗauki matakan sanya ido kan ’ya’yansu tun daga matakin farko, domin hana su shiga aikata munanan ayyuka da ka iya janyo matsalar tsaro.
A nasa jawabin, shugaban ƙungiyar Vigilanti ta jihar Kano, Shehu Rabi’u, ya ce za su ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da tsaro a yankunan da suke aiki, duk da ƙalubalen da suke fuskanta.
Shi ma mai unguwar Rinji Ja’en, Muhammad Sani Rinji, ya ce dalilin shirya taron ya samo asali ne daga yadda wasu matasa ke sayarwa da kuma amfani da miyagun ƙwayoyi a yankin, baya ga yawaitar rahotannin satar kayayyaki da sauran matsalolin da suka shafi tarbiyyar al’umma.
Taron ya samu halartar jami’an tsaro daga hukumomi daban-daban, da malaman addini, da sauran al’umma, inda mahalarta suka cimma matsayar haɗa kai da yin aiki tare domin tsaftace yankin Rinji Ja’en da ke ƙaramar hukumar Gwale.
You must be logged in to post a comment Login