Labaran Kano
Hukumar karbar korafi da yaki da cin hanci ta fara binciken wani da ake zargi da daukar ma’aikatan bogi a Kano

Hukumar Karɓar Korafe-Korafe da Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Kano ta fara bincike tare da kama wani mutum, Adam Aliyu Yahaya, da ake zarginsa da ɗaukar ma’aikata na bogi da ba su shaidar aiki a ma’aikatun gwamnati.
Shugaban Hukumar, Malam Sa’idu Yahaya, ya ce zuwa yanzu sun samu takardar umarnin kotu na kada a tsare shi ko a matsa masa, amma suna jiran hukuncin kotu domin ci gaba da binciken.
Zuwa yanzu Hukumar ta bayyana cewa ba shi da wata alaƙa da Hukumar gwamnati kuma ba jami’inta ba ne.
Sa’idu Yahaya ya yi kira ga jama’a cewa gwamnati ba ta karɓar kuɗi don bayar da aiki, kuma duk wanda ya bayar ko aka ba shi kuɗi ya aikata laifi.
You must be logged in to post a comment Login