Connect with us

Labarai

Rundunar ’yan sanda ta tura jami’ai 250 zuwa kananan hukumomin kan iyaka Kano

Published

on

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta tura jami’ai 250 zuwa kananan hukumomin da ke kan iyakar jihar, domin karfafa tsaro da dakile matsalolin rashin tsaro.

 

Jami’an, wadanda suka kammala wani horo na musamman na tsawon wata guda, za su taimaka wajen gudanar da sintiri da sauran ayyukan tabbatar da tsaro a yankunan.

 

Rundunar ta ce matakin na daga cikin kokarinta na kara yawan jami’an tsaro a wuraren da ke da muhimmanci, domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

 

Rundunar ta kuma bukaci alumma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai, tare da kai rahoton duk wani mutum da ake zargi da barazana ga zaman lafiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!