Labarai
Yan sanda a Kano sun sanya dokar hana zirga-zirga a kananan hukumomi Biyu

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta sanar da hana zirga-zirga a kananan hukumomin Dawakin Kudu da Warawa daga karfe 12 na rana zuwa 5 na yamma ranar Asabar, 20 ga Yuni, 2026, domin tabbatar da zaman lafiya yayin zaben cike gurbin kujerar Majalisar Wakilai.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce jami’an tsaro sun bazu a rumfunan zabe, cibiyoyin tattara sakamako da ofisoshin hukumar zabe domin kare lafiyar jama’a da tabbatar da sahihin zabe. Ya kara da cewa ma’aikatan INEC, masu sa ido kan zabe, ’yan jarida da jami’an da ke kan aiki ne kawai za su samu izinin zirga-zirga a lokacin.
Rundunar ta gargadi masu siyasa da magoya bayansu da su guji sayen kuri’u, tsoratar da masu kada kuri’a, satar akwatin zabe da yada labaran karya. Ta kuma bukaci al’umma su hada kai da jami’an tsaro tare da kai rahoton duk wani abu da zai iya tayar da zaune tsaye domin gudanar da zaben cikin lumana.
You must be logged in to post a comment Login