Labarai
Rundunar Yan sandan Kano ta kama masu aikata laifuka 78 a watan Afrilu

Rundunar Yan sandan Jihar Kano ta tabbatar da kama masu aikata laifuka 78 daga ranar 23 ga watan Afrilun da ya gabata zuwa yau 9 ga watan Mayun da muke ciki.
Kwamishinan yan sandan jihar CP Ibrahim Adamu Bakori ne ya bayyana hakan a zantawarsa da manema labarai.
Ya kuma ce sun samu nasarar kama wani shahararran mai fataucin miyagin kwayoyi dake Unguwar Tudun Yola wato Sulaiman Danwawu da kuma wani shararran mai fashi da makami mai suna Mansur Sani dan karamar hukumar Rogo.
Kwamishinan yan sandan CP Ibrahim Adamu Bakori ya ce an samu raguwar aikata kwacen waya da wasu daga cikin mugan laifuka na fatan Daba.
You must be logged in to post a comment Login