Labarai
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ceto wasu ƴan ƙasar Mali 30

Rundunar ‘yan sandan kasar nan ta ceto wasu ƴan ƙasar Mali 30, da akayi safafar su zuwa birnin tarayya Abuja, sakamakon bayanan sirri da suka samu, da ta ce akwai wasu ‘yan kasashen na Afirka daban a cikin su.
Haka zalika rundunar ta ce ta kama wasu mutane goma sha uku da ake zargi da alaka da kungiyoyin masu aikata laifuka.
Wani bincike da aka gudanar tun daga farko ya nuna cewa kungiyar ta yi wa matasa daga kasashen yammacin Afirka musamman Mali da Gabon romon baka ne da zummar zasu fitar dasu kasahsen Turai da kuma sama musu ayyukan yi mai tsoka a Najeriya.
You must be logged in to post a comment Login