Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina ta dakile hare-haren ’yan bindiga guda biyu a Kananan Hukumomin Kanƙara da Malumfashi tare da kubutar da mutane 12 da aka yi yunkurin garkuwa da su da kuma ƙwato dabbobi 25.
Hakan na cikin bayanin da Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina, DSP Aliyu Abubakar Sadiq, ya wallafa.
Bayanin ya nuna cewa rundunar ta samu nasarar daƙile harin ’yan bindigar.
Haka kuma ya ce, jami’an tsaron sun samu nasarar ƙwato dabbobi 25 da maharan suka yi yunkurin tafiya da su a yayin hare-haren.
Rundunar na ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin Jihar Katsina.
You must be logged in to post a comment Login