Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar ‘yan sandan Zamfara ta ceto mutane 11 da aka yi garkuwa da su

Published

on

Rundunar ‘yan sandan Jihar Zamfara da hadin gwiwar kwamitin zaman lafiya na gwamnatin Jihar sun samu nasarar ceto mutane 11 da masu garkuwa da mutane suka sace a Jihar.

Mai magana da yawun rundunar Muhammad Shehu ya tabbatar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a birnin Gusau.

Muhammad Shehu ya ce an sace mutanen ne a ranar juma’ar da ta gabata, 4 ga wannan wata na Yuni da muke ciki, a kauyen Wanzamai da ke karamar hukumar Tsafe.

Ya kara da cewa kafin sada mutanen da aka ceto da iyalansu sai da aka duba lafiyarsu a asibiti don tabbatar da koshin lafiyarsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!