Connect with us

Labarai

Rundunar ‘yansanda ta gano wurin kera makamai a Yobe

Published

on

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe ta gano wani wurin da ake ƙera bindigu ba bisa ka’ida ba a garin Potiskum tare da kama mutane bakwai da ake zargi da hannu a lamarin.

Hakan  na cikin sanarwar da Jami’in Yaɗa Labaran Rundunar Yobe, SP Dungus Abdulkarim, ya fitar.

Sanarwar ta ce jami’an tsaro sun kai samame ne a wani garejin gyaran karafa da ke Tasha Adua a kan titin Danchuwa bayan samun bayanan sirri kan wasu da ake zargin suna kera bindigogin gargajiya da sauran makamai.

Rundunar ta ce ta kwato bindigogi da aka kera, da wasu sassan bindigogi da kayan aikin da ake amfani da su wajen kera makaman.

Haka zalika, ana ci gaba da bincike domin gano sauran masu hannu a lamarin da kuma masu sayen makaman.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Yobe, Usman Kanfani Jibrin, ya umarci jami’an da ke gudanar da binciken su fadada bincike domin gano sauran wuraren da ake kera makamai ba bisa ka’ida ba a yankin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!