Connect with us

Labarai

Masu garkuwa da mutane sun sace ƙanwar tsohon Ministan Wutar Lantarki

Published

on

Wasu mahara da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi sace ƙanwar tsohon Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, tare da ‘ya’yanta tagwaye biyu a birnin Badun  na Jihar Oyo.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da safiyar yau Laraba a unguwar Elewura da ke yankin Challenge, a ƙaramar hukumar Badun  ta Kudu.

Mai taimaka wa Adelabu a harkokin yaɗa labarai, Femi Awogboro, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce ƙanwar Adelabu tare da tagwayen nata, Peter da Paul, sun fito daga gida lokacin da wasu ‘yan bindiga suka tare su tare da yin garkuwa da su.

A cewarsa, maharan sun kai harin ne ba zato ba tsammani kafin su tafi da waɗanda suka sace zuwa wani wuri da ba a sani ba.

A watan Mayun da ya gabata  an yi garkuwa da malamai da ɗalibai sama da 40 a yankin Ahoro-Esiele na ƙaramar hukumar Oriire, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce kan matsalar tsaro a jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!