Connect with us

Labarai

Sojoji sun hallaka kwamandojin ‘yan ta’adda da karin wasu 50 a Najeriya

Published

on

Rundunar  Sojin kasar nan ta tabbatar da hallaka wasu manyan kwamandojin ’yan ta’adda tare da sama da mayaƙa 50 a hare-haren sama da aka kai a yankin Tafkin Chadi ƙarƙashin aikin Operation Hadin Kai.

 

Majiyoyin tsaro, sun tabbatar kai harin  a ranar 31 ga Mayu a yankunan Kirta da Arina Ciki bayan samun sahihan bayanan sirri kan motsin ’yan ta’addan a wuraren.

 

Rahoton ya ce daga cikin waɗanda aka kashe akwai Khalifa Umar, wani fitaccen mamba a majalisar Shura ta ’yan ta’addan, da wasu kwamandoji biyu masu suna Abdallah da Abduljalil.

 

Baya ga kashe mayaƙan, hare-haren sun lalata cibiyoyin ajiya, wuraren samar da kayayyaki da sauran muhimman gine-ginen da ’yan ta’addan ke amfani da su wajen gudanar da ayyukansu.

 

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa matsin lambar hare-haren sama ya sa da dama daga cikin ’yan ta’addan suka bar maboyarsu da ke tsibiran Tafkin Chadi zuwa wasu wurare da suka fi bayyana a doron ƙasa.

 

Haka kuma, jami’an tsaro sun ce duk da cewa yanayin tsaro a yankin yana bunƙasa, har yanzu ana ci gaba da sanya ido tare da ɗaukar matakan kariya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!