Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sakacin iyaye ne ke kawo rashin tarbiyya -Dakta Zahra’u

Published

on

 

Gwamnatin jihar kano ta danganta matsalolin da ake samu a wannan zamani da tsantsar rashin tarbiyyar da iyaye ke gaza baiwa ‘ya’yansu da kuma yawaitar jefar da yara ake yi.

Kwamishiniyar mata da walawalar jama’a ta jihar Kano, Dakta Zahra’u Muhammad Umar ce ta bayyana hakan ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan Radiyo freedom, wanda ya mayar da hankali kan al’amuran da suka shafi tabarbarewar tarbiyya a wannan lokaci.

Dakta Zahra’u ta ce, wajibi ne iyaye su tashi tsaye wajen inganta tarbiyyar ‘ya’yansu don samun raguwar matsalolin da ake fuskanta a gidajen aure.

Ta kuma kara da cewa, dawo wa kan tafarkin addini zai ragewa iyaye mata matsalolin da suke fuskanta a zamantakewar aure.

Kwamishinyar ta yi kira ga masu hannu da shuni da sarakuna da kuma sauran jama’a da su hada hannu wajen tallafawa gwamnati don ganin an inganta rayuwar mata da kuma kananan yara a jihar Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!