Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Sama da mutum dubu 18 ne ke ɗauke da cutar tarinfuka a Kano – ma’aikatar lafiya

Published

on

Gwamnatin jihar kano ta ce sama da mutane dubu goma sha takwas aka gano masu ɗauke da cutar tarinfuka.

Babban jami’i mai kula da bangaren yaƙi da cutar tarin fuka da kuturta a ma’aikatar lafiya ta Kano Dakta Ibrahim Aliyu Umar ne ya bayyana hakan yayin zantawarsa da freedom radio a wani ɓangare na bikin ranar yaƙi da cutar tarinfuka da ake gudanarwa.

Dakta Ibrahim Aliyu ya kuma ce “Cutar tarinfuka cuta ce da ke yaduwa daga wani zuwa wani ta yadda take shafar huhu kai tsaye wanda hakan ke haddasa matsanancin tari”.

“Illolin cutar kan tsallaka ga sauran sassan jiki da suka haɗa da ƙoda, Hanta, ƙwaƙwalwa da kuma ƙashin baya.”

Ya kuma ce ana gane alamomin cutar tarinfuka ne ta hanyar yawan ciwon kai, gumin dare da kuma yawan jin kasala.

Majalisar ɗinkin duniya ce dai ta ware duk ranar 24 ga watan maris ɗin kowace shekara a matsayin ranar wayar da kan mutane kan cutar tarinfuka.

Taken bikin ranar na bana shi ne ƙara saka tallafi don kawo ƙarshen cutar a fadin duniya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!