Labarai
Samun ƴancin kai ya kawo ci gaba a ɓngaren shari’a – Babajibo Ibrahim
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/11/Kotu.jpg)
Mai magana da yawun kotunan jihar Kano Baba Jibo Ibrahim ya ce, bayan samun ƴancin kai daga turawan mulkin mallaka na Burtaniya Alkalai suma sun samu ƴancin kan su.
A cewar sa tun bayan samun ƴancin kan Ademola shi ne Alƙali na farko ɗan ƙasa daya fara yin sugabanci lauyoyi a kasar na.
Babajibo Ibrahim ya ce, a wancan lokacin karatun lauya sai an je can ƙasashen ƙetare sannan ake yinsa .
“A nan kano ma haka abin yake turawan ke rike da bangaren shari’a sai kuma daga baya aka samar da hukumar shari’a da rukunin kotuna na jihar kano” a cewar Babajibo.
Ya kuma ce an samar da ɓangaren harkokin shari’a a 1968 wanda chif joji na farko shi ne justice Dahiru Mustapha har sai da ya riƙe kotun koli ta tarayya kafin Allah ya yi masa rasuwa .
“Ci gaban da aka samu a yanzu a ɓangaren shari’a a yanzu shi ne samuwar kotuna acikin mutane wanda hakan ne ya samarwa mutane sauki da kuma ƙarin alƙalai sabanin wancan lokacin Kano da Jigawa kotuna basu fi 4 ba Kuma ana shan wahala kafin jama’a su kai korafin su”. in ji Babajibo.
You must be logged in to post a comment Login