Connect with us

Labarai

Sarki Sunusi ll ya bukaci mutane su rika yin koyi da halayen magabata

Published

on

‎Mai martaba sarkin kano khalifa Muhammadu Sunusi ll, ya bukaci al’ummar jihar da su rika yin koyi da kyakkyawan halayen magabata da suka bayar da gagarumar gudunmawar wajen ciyar da jihar Kano gaba.

‎Sarkin  ya bayyana hakan ne a wajen taron kaddamar da littafi mai taken Musan magabatanmu wanda Injiniya Kabiru Ahmad Kwalli ya wallafa Kan irin gagarumar gudummawar da wasu fitattun mutane  a jihar nan suka bayar wajen ciyar da Kano gaba wanda aka gudanar a dakin taro na jami’ar North West dake nan kano.

‎Khalifa Muhammadu Sunusi II, ya yaba da kokarin mawallafin littafin bisa ga hangen nesa da yayi  wajen zakulo mashahuran mutane wadanda suka bada gudummawa a fannoni daban daban na rayuwar  Jama’a.

‎A nata jawabin shugabar jami’ar ta North West Farfesa Amina Salihi Bayero, ta ce littafin zai taimaka musamman ga yara masu tasowa wajen sanin magabata da suka bada gagarumar gudunmawa  wajen hidimtawa al’umma dama kasa baki daya.

Taron, ya samu halartar Farfesa Ibrahim Garba Satatima da Farfesa Abdallah Uba Adamu  da Malam  Ibrahim Khalil inda suka gabatar da mukala.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!