Labarai
Sarkin Zazzau ya kai ziyarar jaje Maraban Jos bisa kisan Ummulkhairi

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya jagoranci wasu daga cikin ‘yan Majalisar Masarautarsa zuwa Maraban Jos domin yi wa iyalan Marigayya Malama Ummulkhair ta’aziyya, wadda aka kashe a wani lamari mai tayar da hankali.
A cewar wata sanarwa da Sashen Yaɗa Labarai na Masarautar Zazzau ya fitar, Sarkin ya bayyana alhininsa da matuƙar jimaminsa kan wannan mummunan al’amari.
Ya kuma miƙa sakon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayiyar tare da kira gare su da su ɗauki wannan jarabawa da haƙuri da kuma yarda da ƙaddarar Allah Maɗaukakin Sarki.
Hakazalika, Sarkin ya yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayiyar kura-kuranta, Ya kuma saka mata da Aljannatul Firdaus.
Mai Martaba Sarkin Zazzau ya kuma yi kira ga al’umma da su kwantar da hankalinsu su jira sakamakon bincike da matakan da gwamnati za ta ɗauka, tare da gujewa ɗaukar doka a hannu domin tabbatar da zaman lafiya da adalci.
You must be logged in to post a comment Login