Labarai
Kotu ta umarnin kai mata hujjojin shari’ar Malam Abduljabbar

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta umarci kotun da ta yanke wa Malam Abduljabbar Nasir Kabara, hukuncin kisa da ta gabatar mata da littattafan da aka yi amfani da su a matsayin hujjoji yayin gudanar da shari’ar.
A zaman kotun na yau Litinin, alkalan kotun ƙarƙashin jagorancin Nasir Saminu da Sanusi Ado Ma’aji, sun saurari ɓangarorin da ke ƙara da waɗanda ake ƙara.
Tun da farko an ba ɓangaren waɗanda ake ƙara damar gabatar da martaninsu, kuma a yau sun yi hakan. Kotun ta saurari bayanan kowane ɓangare tare da karɓar hujjojinsu.
Haka kuma, kotun ta umarci a gabatar mata da littattafan da Malam Abduljabbar ya yi bayani a kansu yayin shari’ar, tare da bayyana cewa za ta sanar da ranar yanke hukunci nan gaba.
You must be logged in to post a comment Login