Connect with us

Labarai

Sarkin Gaya ya bukaci matasa da dalibai su guji tu’ammali da miyagun kwayoyi

Published

on

Mai martaba Sarkin Gaya Dakta Aliyu Ibrahim Abubakar ya yi kira ga matasa da su dalibai dasu guji yin ta’ammali da miyagun kwayoyi tare da  sanya ido a kayan da gwamnati ta samar musanman a fannin ilimi 

 

Sarki n ya bayyana hakane a lokacin da kungiyar dalibai ta kasa rashen karamar hukumar gaya suka kai masa ziyara a fadarsa 

 

Sarkin na Gaya ya kuma ja hankalin  kungiyar daliban da su jajirce wajen neman ilimi domin shine ginshikin rayuwa, haka kuma sarkin ya hori daliban dasu guji shaye shaye da fadan daba  don kyautata rayuwarsu.

 

Daya ke jawabi shugaban kungiyar daliban, Bello Abdullahi Torenke yace makasudun ziyarar shine neman tabariki da kuma ban girma ga mai martaba sarki. 

 

Sarkin gaya dakta Aliyu Ibrahim ya godewa kungiyar daliban bisa wannan ziyara ,tare da yi musu addu’a da fatan alheri.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!